Birbishin Rikici

Bauta A Matsayin Ungozama


Listen Later

Adisu Abba wata mata ce mai shekaru 45 kuma uwa ga ‘ya’ya biyar. Ta fito daga Dikwa, Jihar Borno, a arewa maso gabashin Najeriya. Tun kafin rikici ya tarwatsa rayuwarta, ta riga ta fara koyon aikin da zai zama ginshiƙin rawarta a cikin al’ummarta—ta koyi yadda ake taimaka wa mata wajen haihuwa.

An yi garkuwa da Adisu a hannun ‘yan ta’adda na tsawon shekaru uku,a wannan lokacin, ta taimaka wajen haihuwar jarirai biyar.

A wannan shirin na #BIRBISHINRIKICI, mun bada labarinta da kuma abin da yake nufi yin aikin ungozoma yayin da take tsare a hannun ƙungiyar ta’addanci ta Boko Haram.

...more
View all episodesView all episodes
Download on the App Store

Birbishin RikiciBy HumAngle