Najeriya a Yau

Halin Da Muke Ciki Bayan Rasa ‘Yan Uwanmu A Hadarin Kwale-Kwale A Sakkwato


Listen Later

Send us a text

‘Yan uwan wadanda suka rasa rayukansu a hatsarin jirgin ruwa da ya faru a garin Kojiyo dake karamar hukumar Goronyo a jihar sakkwato sun samu kansu cikin damuwa.


Yayin da kalilan daga cikin wadanda abun ya rutsa dasu suka tsira da ransu, wasu da dama sun mutu, a gefe guda kuma an kasa gano inda sauran da abun ya rutsa dasu suke.

Wannan lamari ya tayar da hankulan jama’a, musamman ‘yan uwan waɗanda abin ya shafa, waɗanda yanzu ke cikin damuwa, jimami da rashin sanin makoma.


Shirin Najeriya  A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan irin halin damuwa da wadanda suka rasa ‘yan uwansu sakamakon kifewar kwale-kwale a garin Kojiyo dake jihar Sakkwato ke ciki.

...more
View all episodesView all episodes
Download on the App Store

Najeriya a YauBy Muslim Muhammad Yusuf, Ummu Salmah Ibrahim