A cikin shirin tambaya da amsa na wannan mako, an karanto wasu daga cikin tambayoyin da wasu daga cikin masu sauraronmu suka aiko, tare da kawo amsoshinsu daidai gwargwadon iko, kamar yadda aka saba a duk mako. Daga cikin tambayoyin da aka kawo muku a cikin shirin, akwai wadda ke neman sanin inda mulkin mallaka ya samo asali, da kuma ko turawa ne kawai suka yi wannan salon mulki. wannan tambayar da ma wasu aka amsa a cikin shirin "Tambaya da Amsa" na wannan mako.