Sign up to save your podcastsEmail addressPasswordRegisterOrContinue with GoogleAlready have an account? Log in here.
A kowace Litinin da Juma'a a shirye-shiryen Safe da Dare ana gabatar da Shirin Duniyar Wasanni akan batutuwa daban-daban da suka shafi wasanni a sassan duniya.... more
FAQs about Wasanni:How many episodes does Wasanni have?The podcast currently has 214 episodes available.
September 29, 2025Mahangar masana game da yadda Dembele ya lashe kyautar Ballon d'Or a banaShirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh ya mayar da hankali kan yadda ɗan wasan gaba na PSG ɗan Faransa Ousmane Dembele ya lashe kyautar Ballon d'Or a bana, bayan nasarar shi ta lashe kofuna da dama cikin kakar da ta gabata da ƙungiyar tasa da ke birnin Paris. Duk da cewa anjima ana hasashen Dembele ya lashe wannan kyauta lura da namijin ƙoƙarinsa a kakar da ta gabata, amma wasu na da ra'ayin cewa sam ɗan wasan bai cancanci wannan kyauta ba. Game da wannan saɓanin ra'ayi, shirin na Duniyar Wasanni ya tattauna da masana a fagen na wasanni waɗanda suka bayyana ra'ayoyinsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin....more10minPlay
September 22, 2025Adawar magoya bayan ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa na ƙarawa gasar armashiShirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan mako ya yi duba ne kan yadda adawar magoya bayan ƙungiyoyi ke karawa kwallon ƙafa tagomashi. Wasanni da dama ne dai ke samu karbuwa a duniya da suka haɗa da kwallon ƙafa da kwallon kwando da kwallon Cricket da Tennis da dai sauransu, amma kuma kowane wasa na da irin nashi magoya baya da suke matuƙar ƙaunarsa da so a duniya. Bincike ya nuna cewa babu wani wasa da ta fi kwallon kafa magoya baya a duniya, inda aƙalla mutane biliyan 3 da rabi ne ke sha'awar wasan baya ga ƴan kwallon kansu da suka kai miliyan 250, waɗanda hukumomin kwallon ƙafa a duniya FIFA ta yiwa rijista. Hatta a Najeriya nuna sha'awa na magoya baya ba ya misaltuwa, domin babu lungu da sako da wasan bai samu karɓuwa ba musamman ma wasannin nahiyar Turai da ya fi can hankali. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin....more10minPlay
September 15, 2025Makomar tawagar Najeriya a ƙoƙarin neman gurbin zuwa gasar lashe kofin duniyaShirin a wanan mako tare Khamis Saleh, ya yi duba ne kan makomar tawagar Najeriya a ƙoƙarin neman gurbin zuwa gasar lashe kofin duniya, inda a tsakiyar makon da ya gabata aka kammala wasannin na 8 na sharen fagen zuwa gasar lashe kofin duniya da ƙasashen Canada da Mexico da kuma Amurka za su karɓi bakunci a shekara mai zuwa. Kawo yanzu dai wasanni sun ɗauki zafi ganin cewa wasu daga cikin tawagogin ƙasashen sun fara jin kanshin halartar gasar, amma kuma wasu har yanzu tana ƙasa tana dabo. Latsa alamar sauri domin sauraron cikakken shirin........more10minPlay
September 08, 2025Yadda wasannin sharen fagen zuwa gasar cin kofin duniya ke gudana a AfrikaKawo yanzu dai wasanni sun ɗauki zafi ganin cewa wasu daga cikin tawagogin ƙasashen sun fara jin kanshin halartar gasar, amma kuma wasu har yanzu tana ƙasa tana dabo. Tawagar ƙasar Morocco tuni ta samu nata tikitin bayan da ta haɗa maki 18, tazarar maki 8 tsakaninta da Tanzania. Tawagogin ƙasashe irinsu Masar da Algeria da Tunisia da Ghana da Afrika ta Kudu, duk da cewa akwai tazarar maki masu ɗan dama tsakaninsu da waɗanda ke mataki na biyu a rukunansu, har yanzu akwai sauran rina a kaba....more10minPlay
September 01, 2025Yadda ake samun takun saƙa tsakanin ƙungiyoyi da 'yan wasa wajen canza sheƙaShirin a wannan makon zayyi duba ne kan yadda ake samun takun saƙa tsakanin ƴan wasa da ƙungiyoyinsu a duk lokacin da suke son sauya sheƙa. A duk lokacin da a ka buɗe kasuwar sayen ƴan wasa a duniya, a kan samu takaddama lokaci zuwa lokaci tsakanin ƴan wasa da kuma ƙungiyoyin su saboda wasu ƙungiyoyi na kin amincewa da ƴan wasansu su sauya sheka lokacin da su kuma ƴan wasan ke son bari....more10minPlay
August 25, 2025Sabon jagorancin ƙungiyar Ranchers Bees na ƙoƙarin farfaɗo da martabartaShirin Duniyar Wasanni a wannan mako ya yi dubu ne kan amsar ragamar jagorancin ƙungiyar Ranchers Bees da ke jihar Kaduna a Najeriya, da ɗan wasan Super Eagles Sadiq Umar Jololo da kuma ɗan majalisar wakilai Hon. Bello El-Rufai suka yi. Ƙungiyar kwallon ƙafa ta Ranchers Bees na cikin ƙungiyoyin kwallon ƙafa da suka yi suna a baya amma a ka daina jin ɗuriyarta a yan shekarun nan, duk kuwa da cewa har a Nahiyar Afrika baki ɗaya ƙungiyar ta yi fice. A baya dai ƙungiyar ta Ranchers Bees ta lashe kofin yankin Afrika ta yamma wato WAFU sannan a Najeriya kuwa ta lashe kofin kalubale FA cup da dama. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.............. ...more10minPlay
August 18, 2025Yadda wasanni suka gudana bayan fara sabuwar kakar ƙwallon ƙafa a TuraiShirin 'Duniyar Wasanni' a wannan makon ya mayar da hankali ne a kan yadda aka fara sabuwar kakar ƙwallon ƙafa a bana a manyan Lig-Lig na sassan nahiyar Turai. Manyan wasannin dai sun haɗa da na Firimiyar Ingila, La Ligar Spain, da kuma gasar Ligue 1 na ƙasar Faransa. Kamar yadda za a ji cikin shirin tare da Khamis Saleh, Liverpool ce ta fara buɗe sabuwar kakar wasa a Firimiyar Ingila inda ta lallasa Bournemouth da ƙwallaye 4-2....more10minPlay
August 11, 2025Yadda wasanni ke ɗaukar hankalin matasa a lokacin hutu a NijarShirin a wannan makon zayyi duba ne kan yanda wasanni ke ɗaukan hankalin matasa a irin wannan lokaci na hutun ƴan makaranta a Nijar. A duk lokacin da aka yi dogon hutun ƴan makaranta a Jamhuriyar Nijar, wanda ke farawa daga watan Yuli zuwa Satumba. Irin wannan lokaci na zama wata babbar dama ga masu kula da ɓangaren wasanni iri daban daban, don suna samun ɗinbin matasa da ke nuna sha’awarsu a ɓangaren wasanni....more10minPlay
August 04, 2025Yadda shugaban Najeriya ya tarbi tawagar Super Falcons bayan lashe gasar WAFCONShirin a wannan makon zayyi duba ne kan karramawar da gwamnatin Najeriya ta yi wa tawagar Super Falcons na lashe gasar WAFCON. A makon da ta gabata ne shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya karrama ƴan wasan tawagar ƙungiyar kwallon ƙafa ta mata ta ƙasar Falcons, bayan nasarar lashe kofin WAFCON karo na 10 daga cikin 13 da aka yi. Cikin kyautukan da gwamnati ta baiwa waɗannan ƴan wasa akwai lambar girmamawa na ƙasa wato OON da shugaban Tinubu ya baiwa dukkan ƴan wasan da masu horar dasu, hakazalika kowacce ƴar wasa ta samu dalan amurka dubu 100, da kuma karin naira miliyan goma-goma daga ƙungiyar gwamnonin Najeriya. Tuni dai shugaban hukumar wasani a Najeriya Shehu Dikko ya yaba da wannan nasarar da kuma irin karramawar da shugaban ƙasar ya yiwa ƴan wasan. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh....more10minPlay
July 28, 2025Yadda ta kaya a gasar lashe kofin Afirka ta mataShirin Duniyar Wasanni a wannan makon tareda Khamis Saley yayi duba ne kan wasan ƙarshe na gasar lashe kofin mata ta Afrika WAFCON da aka yi a ƙarshen mako. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.........more10minPlay
FAQs about Wasanni:How many episodes does Wasanni have?The podcast currently has 214 episodes available.