Sign up to save your podcastsEmail addressPasswordRegisterOrContinue with GoogleAlready have an account? Log in here.
A kowace Litinin da Juma'a a shirye-shiryen Safe da Dare ana gabatar da Shirin Duniyar Wasanni akan batutuwa daban-daban da suka shafi wasanni a sassan duniya.... more
FAQs about Wasanni:How many episodes does Wasanni have?The podcast currently has 231 episodes available.
November 17, 2025Yadda ta kaya a karawar da aka yi tsakanin Najeriya da DR CongoShirin Duniyar Wasanni a wannan lokaci ya yi duba ne kan yadda wasan ƙarshe na nemon gurbin wakiltar Afrika a matakin duniya, wajen samun tikin zuwa gasar lashe kofin duniya ya gudana tsakanin Najeriya da Jamhuriyar Dimukaraɗiyyar Congo. Karawar da suka yi a filin wasa na Moulay Abdellah da ke birnin Rabat, ta kai matakin dugun daga kai sai mai tsaron gida bayan da suka tashi 1-1. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh...............more10minPlay
November 10, 2025Yadda aka fafata a gasar kofin Sardauna ta tsoffin 'yan wasan arewacin NajeriyaShirin Duniyar Wasanni na wannan mako ya mayar da hankali ne kan gasar da tsofaffin ƴan wasan Najeriya da suka fito daga jihohin Arewacin ƙasar suka fafata. A makon daya gabata ne garin Maiduguri babban birnin jihar Borno, ya karɓi baƙuncin gasar kofin Sardauna karo na 13, wacce tsofaffin ƴan wasan da suka fito daga jihohi 19 na Arewacin Najeriya suka ƙirƙira da zummar sada zumunci da kuma haɗa kan jihohin arewacin ƙasar. Tawagar da ta wakilci jihar Kebbi a wannan gasa ce dai ta yi nasarar lashe wannan kofi, bayan da ta doke takwararta ta Kano a bugun daga kai sai mai tsaron gida da ci 4-3. Latsa alamar sauti don sauraren shirin tare da Khamis Saleh......more10minPlay
November 03, 2025Karo na biyu a jere Alƙalan wasan Najeriya sun gaza samun wakilci a AFCONShirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan makon ya mayar da hankali kan yadda Najeriya ta gaza samun gurbin alƙalin wasanni a gasar AFCON karo na biyu a jere. A ƙarshen watan da ya gabata ne hukumar ƙwallon ƙafar Afrika CAF ta fitar da jadawalin alƙalan wasanni da za su bayar da gudunmawa a gasar cin kofin ƙasashen Afrika ta AFCON da zata gudana a Morocco cikin watan gobe, amma ba tare da alƙalin wasa ko guda ɗaya daga Najeriya ba. Ko a makamanciyar gasar da ta gabata a Ivory Coast cikin shekarar 2024 babu wakilcin ko da alƙalin wasa guda daga Najeriyar, lamarin da ke matsayin babban koma baya ga wannan ƙasa ta tayi shura a fagen ƙwallo. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin......more10minPlay
October 27, 2025Yadda Real Madrid ta doke Barcelona da ƙwallo 2 da 1 a haɗuwar El ClassicoShirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan mako ya nazarci yadda aka yi fafatawa mai cike da armashi tsakanin Barcelona da Real Madrid wato haɗuwar hamayya tsakanin manyan ƙungiyoyin na Spain guda 2 karawar da ake kira El-Classico. Yayin haɗuwar ta wannan karo dai, Real Madrid ce ta yi nasara da ƙwallaye 2 da 1 duk da ya ke wasan ya gudana ne a gidanta wato filinta na Santiago. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin....more11minPlay
October 20, 2025An fara gasar Super Ligue ta Jamhuriyar NijarShirin duniyar wasanni na wannan mako zai maida hankali a kan yanda aka fara gasar ligue ta ƙasar Niger da ake ma lakabi da SUPER LIGUE. A ƙarshen mako ne aka faro gasar Lik ta Jamhuriyar Nijar wacce ake wa laƙabi da Super Ligue.Ita dai wannan gasa ta Super League ta kasance kololuwar gasar kwallon ƙafa a ƙasar, inda ta ke ƙumshe da ƙungiyoyi 16, kuma babban birnin ƙasar Niamey ka dai na da club 12. A tsarin wasan kowa zai kara da kowa a gida da waje kamar yanda ake yi a sauran ƙasashe ke nan kowace ƙungiya za ta yi wasa 30. Haka kuma kamar a sauran ƙasashe zakaran da ta lashe wannan gasar za ta wakilci ƙasar a gasar ligue a matakin nahiyar Afrika da hukumar Caf ke shirya, don haka ɗaukacin waɗannan club ɗin ke maida hankali don ganin sun taka rawar gani a gasar. Kafin mu tsunduma cikin shirin bari muyi ratse don yin ɗaurayar yadda gasar ta gudana a bara tare da Magaji Minista mai sharhi ne kan harakar wasannin kwallon kafa....more10minPlay
October 13, 2025Makomar ƙasashen Najeriya, Senegal da Afrika ta Kudu a gasar cin kofin DuniyaShirin a wannan mako ya mayar da hankali ne kan wasannin neman tikitin zuwa gasar cin kofin Duniya ta 2026 da ƙasashen Amurka, Mexico da Canada za su karɓi baƙunci. A Nahiyar Afrika tuni dai wasu ƙasashe suka sami tikitin zuwa gasar da suka haɗar da Morocco da Tunisia da Aljeriya da Ivory Cost, sai dai ƙasashen Najeriya da Afrika ta Kudu da kuma Senegal na cikin halin rashin tabbas, sai dai a wannan Talata ne za su san makomarsu. Latsa alamar sauti don sauraron shirin tare da Abubakar Isah Ɗandago.....................more10minPlay
October 06, 2025Gudummawar da cibiyoyin horar da matasa ke baiwa ƙwallon Ƙafa a NajeriyaShirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan lokaci za yi duba ne kan irin gudummawar da cibiyoyin horar da matasa wasan kwallon Ƙafa ke bayarwa wajen zakulo matasan ƴan wasa da horar da su a Najeriya. A wani bangare na gudummawarsu ga ci gaban wasan kwallon kafa a Nigeria, ɗai-ɗaikun jama’a da ƴan kasuwa kai harma da tsofin ƴan wasan tawagar Super Eagles ta ƙasar, sun fara kafa cibiyoyi masu zaman kan su, da su ke zakulowa tare da horar da matasa don yin fice a harkar ta kwallon ƙafa. Irin wadannan cibiyoyin horar da matasa wasan na kwallon kafa da a turance ake kira FOOTBALL ACADEMY, kan shiga birane da karkara don tuntubar ƙanana da matsakaitan club-club, domin samun ƴan wasan daga wajen su da za a yi rijistarsu a wannan cibiya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.....more10minPlay
September 29, 2025Mahangar masana game da yadda Dembele ya lashe kyautar Ballon d'Or a banaShirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh ya mayar da hankali kan yadda ɗan wasan gaba na PSG ɗan Faransa Ousmane Dembele ya lashe kyautar Ballon d'Or a bana, bayan nasarar shi ta lashe kofuna da dama cikin kakar da ta gabata da ƙungiyar tasa da ke birnin Paris. Duk da cewa anjima ana hasashen Dembele ya lashe wannan kyauta lura da namijin ƙoƙarinsa a kakar da ta gabata, amma wasu na da ra'ayin cewa sam ɗan wasan bai cancanci wannan kyauta ba. Game da wannan saɓanin ra'ayi, shirin na Duniyar Wasanni ya tattauna da masana a fagen na wasanni waɗanda suka bayyana ra'ayoyinsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin....more10minPlay
September 22, 2025Adawar magoya bayan ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa na ƙarawa gasar armashiShirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan mako ya yi duba ne kan yadda adawar magoya bayan ƙungiyoyi ke karawa kwallon ƙafa tagomashi. Wasanni da dama ne dai ke samu karbuwa a duniya da suka haɗa da kwallon ƙafa da kwallon kwando da kwallon Cricket da Tennis da dai sauransu, amma kuma kowane wasa na da irin nashi magoya baya da suke matuƙar ƙaunarsa da so a duniya. Bincike ya nuna cewa babu wani wasa da ta fi kwallon kafa magoya baya a duniya, inda aƙalla mutane biliyan 3 da rabi ne ke sha'awar wasan baya ga ƴan kwallon kansu da suka kai miliyan 250, waɗanda hukumomin kwallon ƙafa a duniya FIFA ta yiwa rijista. Hatta a Najeriya nuna sha'awa na magoya baya ba ya misaltuwa, domin babu lungu da sako da wasan bai samu karɓuwa ba musamman ma wasannin nahiyar Turai da ya fi can hankali. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin....more10minPlay
September 15, 2025Makomar tawagar Najeriya a ƙoƙarin neman gurbin zuwa gasar lashe kofin duniyaShirin a wanan mako tare Khamis Saleh, ya yi duba ne kan makomar tawagar Najeriya a ƙoƙarin neman gurbin zuwa gasar lashe kofin duniya, inda a tsakiyar makon da ya gabata aka kammala wasannin na 8 na sharen fagen zuwa gasar lashe kofin duniya da ƙasashen Canada da Mexico da kuma Amurka za su karɓi bakunci a shekara mai zuwa. Kawo yanzu dai wasanni sun ɗauki zafi ganin cewa wasu daga cikin tawagogin ƙasashen sun fara jin kanshin halartar gasar, amma kuma wasu har yanzu tana ƙasa tana dabo. Latsa alamar sauri domin sauraron cikakken shirin........more10minPlay
FAQs about Wasanni:How many episodes does Wasanni have?The podcast currently has 231 episodes available.