2026-03-14
BBC Hausa
Shirin Safe (2:00am EST)
* Shugaba Trump ya ce Amurka ta kai hare-hare a kan abin da ta kira wurare na soja a tsibirin Kharg, babbar tashar fitar da man Iran a tekun Fasha. (Labari mai alaƙa: DWHausa Safe #6)
* Ma’aikatar lafiya ta Lebanon ta ce aƙalla ma’aikatan lafiya goma sha biyu (12) aka kashe a wani hari da Isra’ila ta kai kan wani a ƙaramin asibiti a kudancin ƙasar.
* Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya, ta gargaɗi ƴan ƙasar musamman a jihohin Arewa game da yiwuwar ɓarkewar cutar sanƙarau yayin da aka fara shiga yanayin tsananin zafi.
* Ƙwayar cutar da ta fi sa sankarau din annoba shine ake samu mafi yawan ci a kusan arewacin Najeriya. In haka ya faru, sai mu yi ta bawa mutane ƙanana-ƙananan shawara na kar su [???]. Ba wani cunkoso, a dinga buɗe windo, sannan mu dinka sa mutane suna ɗan wanke baki da drip.
* (A filin Gane Mini Hanya) Har wa yau a Najeriya, majalisar dattawan ƙasar ta ce za ta sake gayyatar shugabancin kamfanin mai na ƙasar: NNPC, kan yadda wasu maƙudan kuɗaɗe suka yi ɓatan dabu a tsakanin shekarar ta 2017 zuwa 2023.
* Yaya ma za a yi a ce tiriliyan ɗari biyu da goma (210T) sun ɓace ko an rasa su, ba a bamu ƙididdiga da ta gamsar da mu ba? A ina kuka kashe su? A me kuka kashe?
* Mai gabatarwa: BBC Hausa Muhammad Annur Muhammad
DW Hausa
Shirin Safe (2:30am EST)
* Mai gabatarwa: DW Hausa Mohammed Tijjani Hassan
* (A shirin Sharhunan Bayan Labarai) A Najeriya, wata cibiyar samar da zaman lafiya ta horas da masu bukata ta musamman kan matakai da hanyoyin da za su bi domin kare kansu a yanayin rashin tsaro da kuma faɗace-faɗace.
* Yayin da a gefe guda, kungiyoyin kare muhalli suka fara gangamin wayar da kan al’umma domin dakile ambaliyar wato ambaliyar ruwa a arewacin Nijeriya.
* A Nijar kuwa sabuwar taƙaddama ce ta kunno kai a tsakanin gwamnati da shugabannin ƙasashen Turai kan buƙatar da suka sake miƙawa ta sakin hamɓararren shugaban ƙasar Mohamed Bazoum wanda ake tsare da shi yau kusan shekaru biyu.
* A Ghana kuwa za a ji ƙarin bayani kan wani tsari da aka samar wanda ya tanadi kare yara daga hatsarin da ke tattare da haƙar ma’adinai ta bayan fage wato Galamsey.
* Trump ya ce Iran ta faɗi a yaƙi kuma a yanzu haka tana son a cimma yarjejeniya. (Labari mai alaƙa: BBCHausa Safe #1)
* An kai hari kan ofishin jakadancin Amurka da ke Iraqi a wannan safiya ta Asabar.
* Wani gagarumin harin Rasha ya yi ajalin mutane biyu a yankin Kiev na Ukraine.
2026-03-13
RFI Hausa
Labaran RFI Hausa na ƙarfe 5 na yamma agogon Najeriya da Nijar 13-03-2026… • RFI Hausa
* Mai gabatarwa: RFI Hausa Shamsiyya Haruna
* An ji ƙarar fashewar abubuwa masu yawa a tsakiyar birnin Tehran dai dai lokacin da ake ci gaba da ƙidayar waɗanda suka mutu a Isra’ila sakamakon harin Iran.
* Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince a sayi ƙarin makamai na zamani domin ƙarfafa gwiwar sojojin ƙasar wajen yaƙi da ƴan ta’adda.
* Senegal na sake nazartar yarjejeniyoyin haƙar iskar gas da man fetur da ƙasar ta ƙulla da kamfanonin ƙasashen waje.
BBC Hausa
Shirin Safe (2:00am EST)
Me ya sa magana kan yaƙin Isra’ila da Iran ta zama laifi a Najeriya?[13][14]
* Ƙungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta zargi hukumar tsaro ta farin kaya a Najeriya DSS da nuna bangaranci wajen kama masu bayyana ra’ayansu akan yakin na Amurka da Isra’ila da suke yi da Iran a Najeriya.
* Salo ne da yake nuna cewa ana nuna kamar bambanci a tsakanin ‘yan Najeriya. Zaka ga cewa akwai waɗanda suke sukan ɗaya ɓangaren da ake yaƙi da shi amma ba ka taɓa ji an kama wani a cikinsu ba. Kaman nan gaba ɗayansa a arewacin Najeriya ake yin sa.
This is a public episode. If you would like to discuss this with other subscribers or get access to bonus episodes, visit hausa.substack.com