Shirin Ilimi Hasken Rayuwa ya tattauna ne da da mashahurin malamin Lissafi, Farfesa na farko a yankin arewa maso yammacin Najeriya kan tsagwaron ilimin lissafin. A cikin shirin za ku ji ayyukan Farfesan da suka shafi lissafin Sallah a rayuwar musulmi da kuma ma’aunin da ya samar ta hanyar ilimin lissafi wajen rabon gado. Sannan shirin ya ji wasu ayyukansa kan daliban Firamare da Sakandare.