Sign up to save your podcastsEmail addressPasswordRegisterOrContinue with GoogleAlready have an account? Log in here.
A kowace Litinin da Juma'a a shirye-shiryen Safe da Dare ana gabatar da Shirin Duniyar Wasanni akan batutuwa daban-daban da suka shafi wasanni a sassan duniya.... more
FAQs about Wasanni:How many episodes does Wasanni have?The podcast currently has 578 episodes available.
March 02, 2026FIFA za ta jagoranci koyar da ƙwallon ƙafa a makarantun NijarShirin “Duniyar Wasanni” tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zai yi duba ne kan yadda aka sanya tsarin koyar da wasan kwallon ƙafa a makarantun Boko na Jamhuriyar Nijar. A wannan makon mun yi dubi ne kan shirin koyar da wasan kwallon ƙafa da za a sirka a tsarin koyarwa a makarantun Boko a Jamhuriyar Nijar, a ƙoƙarin da ake yi na haɓɓaka harkar, ganin yanda take a baya sosai a jadawalin ƙasashe da hukumar kwallon ƙafa ta duniya FIFA ta fitar inda Nijar ɗin ta ke a mataki na 111. Shi dai wannan tsarin, ya kasance wani shiri ne na haɗin gwiwa da aka yi tsakanin hukumar FIFA da kuma gwamnatin Nijar wanda hukumar kwallon kafa ta ƙasar fenifoot ke kula da shi. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin....more10minPlay
February 23, 2026Yadda ta wakana a gasar tseren dawaki da ta gudana a garin Daura na jihar KatsinaShirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan mako ya mayar da hankali ne kan gasar tseren dawaki da aka gudanar a garin Daura da ke jihar Katsina da ke a arewacin Najeriya. A farkon watan Faburairun wannan shekarar ne aka kammala babbar gasar tseren dawaki ta ƙasa da ƙasa da ƙungiyar sukuwar dawaki ta Najeriya ke shiryawa. Wannan ne dai karo na uku da ake gudanar da irin wannan sukuwa a cikin wannan shekarar, bayan da aka yi ta farko a birnin Katsina sai garin Hadeja na jihar Jigawa ya karbi bakunci sannan aka kamma sukuwan zangon farko na wannan shekarar a Daura. Mahaya daga Jihohin Kano da Sokoto da Neja da Bauchi da Kebbi da Katsina, waɗansu daga Jamhuriyar Nijar da Kamaru da Mali da Chadi da kuma Burkina Faso, suka halarci gasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin....more10minPlay
February 16, 2026Taƙaddamar da ta dabaibaye gina filin wasa a jihar Kebbi ta NajeriyaShirin Duniyar Wasanni na wannan mako, ya mayar da hankali ne kan taƙaddamar da ta dabaibaye gina filin wasa a jihar Kebbi ta arewacin Najeriya. Latsa alamar sauti don sauraren shirin tare da Khamis Saleh......more10minPlay
January 26, 2026Gasar tseren dawakai da aka gudanar a jihar Jigawan NajeriyaShirin a wannan lokaci zayyi duba ne kan gasar tseren dawaki da aka gudanar a jihar Jigawa da ke Arewacin Najeriya....more10minPlay
January 19, 2026Senegal ta lashe gasar AFCON karo na biyu bayan nasarar da ta samu kan MoroccoA jiya Lahadi ne dai aka buga wasan ƙarshe a gasar lashe kofin nahiyar Afrika ta AFCON karo na 35 da ƙasar Morocco ta karɓi baƙunci, inda Senegal ta samu nasara da ci 1 da nema kan Morocco, bayan da ɗan wasanta Pape Alassene Gueye ya jefa kwallo jim kaɗan bayan ƙarin lokacin. Wasan ƙarshen ya kasance mai cike da cecekuce sakamakon tsaiko minti 20 da aka samu, sanadiyar bugun daga kai sai mai tsaron gida da aka bai wa Morocco, lamarin da ya fusata ƴan wasan Senegal ficewa daga fili, amma daga baya Sadio Mane ya dawo da su aka ci gaba da fafatawa. Ɗan wasan gaba na Senegal Sadio Mane ne ya lashe gwarzon ɗan wasa a wannan gasa, Yassine Bounou na Morocco ya lashe gwarzon mai tsaron raga shima abokin wasansa Brahim Diaz da ya zubar da bugun daga kai sai mai tsaron gida ya lashe kyautar takalmin zinari da kwallaye 5. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh...............more10minPlay
January 12, 2026Super Eagles ta nuna bajinta a wasan ta da Aljeriya a gasar AFCONShirin Duniyar Wasanni na wanan mako tare da Khamis Saley ya yi dubi kan nasarar da tawagar Najeriya ta samu a wasan dab da na kusa da na ƙarshe a gasar AFCON da ake gudanarwa a kasar Morocco. Shiga alamar sauti domin sauran cikakken shirin........more10minPlay
January 05, 2026Yadda aka doka wasu daga cikin wasanni ƴan zagayen 16 a gasar AFCONShirin Duniyar Wasanni na wannan makon tare da Khamis Saleh ya yi duba kan yadda aka dawo da buga wasanni a zagayen ƴan 16 a gasar AFCON da ke gudana a Morocco a karshen mako. a Danna alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.........more10minPlay
December 29, 2025An kammala gasar kokowa ta ƙasa mafi girma a Jamhuriyyar NijarShirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zayyi duba ne kan yadda aka kammala gasar kokuwar gargajiya ta ƙasa a Jamhuriyar Nijar. Jiya Lahadi ne aka kammala gasar kokowar gargajiya ta ƙasa a Jamhuriyar Nijar da aka gudanar a garin Tawa, wacce ita ce karo ta 46, inda mai masaukin baki ta lashe takobin bayan ƴan kokowarta biyu sun kai wasan ƙarshe a wannan gasa. Bayan karawa ta mintuna 11 da daƙiƙu 6, Nura Hassan ne ya yi nasara kan Zakiru Zakari. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin....more10minPlay
December 22, 2025Yadda aka yi bikin buɗe gasar cin kofin Afrika ta AFCON a MoroccoShirin "Duniyar Wasanni" tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zay yi duba ne kan yadda aka faro gasar lashe kofin nahiyar Afrika da ƙasar Morocco ke karɓar baƙunci. A daren jiya lahadi ne dai aka buɗe gasar lashe ƙofin nahigar Afrika ta AFCON karo na 35 da ƙasar Morocco ke karɓar baƙunci. An dai buga wasanni tsakanin Morocco da Comoros, inda Moroccon ta samu nasasara da ci 2 da nema, wani abu da ke nuna cewa ta faro gasar da ƙafar dama, bayan da Yariya Moulay Hassan bin Mohammed ya buɗe ta tare da rakiyar shugaban hukumar kwallon ƙafa ta duniya FIFA Gianni Infantio da kuma shugaban hukumar kwallon ƙafar Afrika CAF Patrice Motsepe. Ɗan wasan gaba na tawagar Morocco Brahim Diaz da ke bugawa Real Madrid ne ya fara jefa kwallo a raga a minti na 55, kafin Ayoub El Kaabi na ƙungiyar Olympiacos da ya shigo daga baya ya ƙara a minti na 74. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin....more10minPlay
December 15, 2025Taƙaitaccen tarihi kan yadda aka faro gasar AFCON a shekarar 1957Shirin Duniyar Wasanni a wannan lokaci tare da Khamis Saleh ya yi duba ne kan tarihin gasar lashe kofin Afrika AFCON da hukumar CAF ke shiryawa. An faro buga gasar lashe kofin nahiyar Afirka, wacce ke zaman gasar kwallon ƙafa mafi girma da daraja a nahiyar a shekarar 1957, da hukumar kula da kwallon ƙafar Afrika CAF ce ta jagoranci. An fara gudanar da gasar ne a watan Fabrairun shekarar 1957 a birnin Khartoum na ƙasar Sudan da ƙasashe 3, kafin a shekarar 2019 aka faɗaɗata zuwa tawogogun ƙasashe 24, kuma Masar ce ta fara lasheta bayan lallasa Sudan da ta karbi baƙunci a wasan karshe, inda ta lashe kofin da aka sanya masa sunan Abdel Aziz Abdallah Salem, ɗan ƙasar Masar da ya fara shugabantar hukumar CAF. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin....more10minPlay
FAQs about Wasanni:How many episodes does Wasanni have?The podcast currently has 578 episodes available.