Shirinmu na Kasuwa a Kai miki Dole na wannan mako ya tattauna ne akan yadda habakar tattalin arziki kasa ke da nasaba yadda mutanen kasa ke gudanar da harkokinsu na kasuwanci, musamman ta hanyar yin amfani da kudaden kasarsu. A Jihar Diffa dake Nijar, al’umomin kasar sun fi amfani ne da kudaden Najeriya da na Chadi dake makwabtaka da kasar kamar yadda za ku ji a wannan shiri da Nasiruddeen Muhammad ya jagoranta.