A yau juma'a shugaban hukumar kwallon kafar Afrika ,Ahmad Ahmad zai tattaunawa da sashen faransanci na rediyon Faransa RFI, da niyar kawo karin haske dangane da matakin da hukumar ta dau na canza kasar da zata karbi bakuncin gasar cin kofin Afrika na Shekara ta 2019.
A cikin shirin Duniyar Wasanni,Abdoulaye Issa ya samu tattaunawa da masu sharhi dangane da batutuwan da suka jibanci kwallon kafa a Afrika.