Ashekarar bana an huskanci matsalolin ambaliyar ruwa a sassa daban daban na fadin Duniya, wadda tafi kamari dai itace ambaliyar da aka samu a kasar Pakistan wadda ta shafi fiye da mutum miliyam ashirin da daya.
Bayaga wannan ma an samu ambaliyar a yankuna da dama na kasashen nahiyar Africa ciki kuwa, hadda Nigeriya da jamhuriyar Niger.
Ambaliyar da aka samu a jihar Sakkwato dake arewacin Nigeriya, takai ga katsiye muhimmam hanyoyin dake sada kananan hukumomin jihar guda bakwai da babban birnin jihar, itama jami'ar Usmanu dan fodiyo, ta rufe, sakamakon katsiyewar gadar.Gadai rahoton wakilin mu a Sakkwato Faruk Muhammad Yabo.