Yayin da aka shiga cikin gasar Olympics ta 2016 gadan gadan a birnin Rio na Kasar Brazil, shirin ya tattauna da Masana da kuma masu ruwa da tsaki kan harkar wasanni game da tasirin kalubalen da kasar Brazil ke fuskanta zai yi wajen rage armashin gasar.
Filin na Duniyar wasanni ya tattauna da Tsohon dan wasan Super Eagles Garba Lawal, da kuma Aminu Sani Sado mai sharhi kan al'amuran wasanni.