A cikin shirin Duniyar wasanni,mun samu tattaunawa da wasu mata dake sha'awar kwallon kafa,mutanen da suka bamu nasu sani dangane da gasar cin kofin Duniya ta kwallon kafa dake gudana a Faransa yanzu haka.
A cikin shirin mun nemi ji ta bakin Abdoulaye Hassane da ya taba rike mukamin shugabancin hukumar kokowa a Nijar ,wanda ya mana nazari a kai.