Shirin Duniyar Wasanni na wannan makon tare da Ahmed Abba ya tattauna ne game da nasarar da Senegal ta samu ta kasancewa kasa ta farko daga Afrika da za ta karbi bakwancin gasar Olympics ta Matasa a shekarar 2022. Kasar ta doke Najeriya da Botswana da Tunisia da suka yi takarar neman izinin daukan nauyin gasar.Kazalika shirin ya tattauna game da gasar neman gurbin shiga gasar cin kofin Afrika.